Gidauniya ta ruwaito cewa gwamnatin jihar Kano a karkashin Abba Kabir Yusuf ta dakatar da albashin ma’aikatan gwamnati su dubu 10 wadanda gwamnatin Abdullahi Ganduje ta dauka gaf da barinta gwamnati.
Sarkin Noman Gaya Ya Nemi Gwamna Abba Ya Bullo Da Sabon Tsarin Bunkasa Noma
Ban Yi Nadamar Rusau A Kano Ba -Gwamnan Kano
Da suke magana a yayin tattaunawa da ‘yan jarida a ofishin kwamishinan yada labarai jiya, shugaban ma’aikatan ya ce, matakin da aka dauka na dakatar da biyan albashin an yi bisa dacewa da tsari da ka’idoji ma’aikata.
A cewarsa an kafa babban kwamitin da zai yi binciken kwakwaf kan sahihancin takardu da kuma matakai da hanyoyin da aka yi wajen daukan ma’aikatan aiki ‘yan watanni kalilan da karewar wa’adin mulkin tsohon gwamna Dakta Abdullahi Umar Ganduje.
Usman Bala ya ce, babu wani matsala za su dawo da biyan ma’aikatan da aka tantance aka tabbatar da ingancinsu musamman wadanda aka gano suna da sahihan takardu ba wai wadanda aka dauka aiki bisa alfarma ko wata manufa ta daban ba.