Ranar Talala Za A Fara Dawo Da Alhazan kasar nan

Gidauniya Global TV and Radio > News > News > Ranar Talala Za A Fara Dawo Da Alhazan kasar nan
  • Posted by: Gidauniya FM Kano

DAGA NUSAIBA ABDULLAHI TUKUNTAWA

 

A ranar Talata, 4 ga watan Yulin nan a za a fara kwaso alhazan Najeriya zuwa gida.

Hukumar Aikin Hajji ta Ƙasa (NAHCON) ta sanar da cewa ana sa ran kammala kwaso alhazan 95,000 ranar 3 ga watan Agusta.

Kwamishinan hukumar mai kula da sufurin jiragen sama, Goni Sanda ne ya sanar da haka a taron bitar aikin hajjin bana, wanda ya gudana a birnin Makkah.

Tuni dai hukumar ta fara raba wa alhazai manyan jakunkuna, gami da sanarwar fara awon kaya, wanda ta ce nan ba da jimawa ba za a rufe.

A yayin taron ne shugaban tawagar likitocin Najeriya, Dokta Usman Galadima ya sanar da rasuwar alhazan Najeriya hudu a ranar Arafa, wanda hakan ya kara yawan alhazan da suka rasu zuwa 13

 

Author: Gidauniya FM Kano

Leave a Reply